✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

2023: Ina da yakinin za a yi sahihin zabe —Jega

Jega ya ce yana da yakinin Najeriya za ta gudanar da sahihin zabe a 2023 duk da kalubalen da take fuskanta.

Tsohon shugaban Hukumar Zabe ta Kasa(INEC), Farfesa Atahiru Jega, ya ce yana da yakinin Najeriya za ta gudanar da sahihin zabe a 2023 duk da kalubalen da take fuskanta. 

Jega ya bayyana hakan ne a wajen taron karrama Farfesa Adele Jinadu da aka gudanar a Abuja.

Ya ce, duk da hare-haren da ake kai wa cibiyoyin INEC da kuma tashin-tashinar yakin neman zaben da ake gani, yana da tabbacin hakan ba zai hana gudanar da ingantaccen zabe ba a badi.

Ya kara da cewa, duk da dai yana ji wa sakamakon zaben tsoro, amma yana da yakinin a kan makomar kasar.

Haka nan, ya ce duk da abubuwa marasa dadi da wasu shugabannin siyasa ke jagorancin aikatawa, yana fatan tsabtataccen zabe zai samu a kasar a 2023.

(NAN)