✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

2023: Ina nan ina jiranka mu fafata — Tinubu ga Atiku

Sai dai ya ce Atiku da PDP ba su da abin da za su fada wa ’yan Najeriya

Jagoran jam’iyyar APC na kasa kuma mai neman takarar Shugaban Kasa a jam’iyyar, Bola Tinubu, ya taya tsohon Mataimakin Shugaban Kasa murnar lashe zaben fid da gwanin jam’iyyar PDP, inda ya ce yana nan yana jiran shi su fafata.

Ya bayyana haka ne a sakonsa na taya murna ga Atikun, jim kadan bayan an ayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben na ranar Asabar.

Atiku dai ya samu nasarar samun tikitin takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar PDP ne da aka gudanar a filin wasa na Moshood Abiola da ke Abuja.

Tinubu dai ya yaba wa Atiku saboda kishin kasarsa da kuma yadda ya jajirce wajen ganin Najeriya ta kai ga tudun-mun-tsira, tare da yaba wa ragowar ’yan takarar kan yadda zaben ya gudana lami lafiya.

Sai dai Tinubu ya ce yana sa ran fafatawa da Atikun a babban zabe mai zuwa matukar daliget din APC suka zabe shi a zaben da za a yi a makon nan.

Ya ce nasarar Atikun ba ta zo masa da ba-zata ba, la’akari da gogewarsa da kuma gwagwarmayar shi a fagen takarar Shugaban Kasa tun a shekarar 1993.

Ya ce, “Yayin da muke tunkarar babban zabe mai zuwa, ina kira ga dan takarar PDP da ma ragowar ’yan takara da a yi siyasa ba da gaba ba.

“Sai dai PDP ta yi rashin sa’a, ita da dan takararta ba sai sun bata wa kansu lokacin bayanin me zai sa a zabe su ba, bayan sun lalata shekara 16 babu wani abin a-zo-a-gani.

“’Yan Najeriya na sane da irin badakalar da PDP ta tafka a shekara 16, kuma wannan zai yi matukar kawo wa kamfen dinsu tarnaki.

“Amma duk da haka, ina taya tsohon Mataimakin Shugaban Kasarmu murnar lashe zaben a jam’iyyarsu,” inji Tinubu.