✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

2023: Tinubu ya amince zai dauki Musulmi abokin takara —Ganduje

Daukar Musulmi abokin takara ba wani abu ba ne sabo a Najeriya.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na Jihar Kano, ya ce dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ya amince zai dauki Musulmi a matsayin abokin takararsa.

Ganduje ya bayyana haka ne a yayin wata ziyara da manyan malaman jihar kusan 100 suka kai masa ranar Juma’a a gidan gwamnatin jihar.

Ganduje ya ce “Mun ba shi shawara ya dauki Musulmi a matsayin mataimaki kuma ya amince, saboda ba wani abu ba ne sabo a Najeriya.”

Ya kuma yi kira ga taron malaman da su rika yi wa Tinubu addu’o’in samun nasara a zaben 2023.

A yayin da ya mika kokon barar addu’o’in samun zaman lafiya da ci gaba a Jihar Kano, Ganduje ya kuma bukaci malaman da su yi wa mataimakinsa kuma dan takarar gwamnan Kano na jamiyyar APC a zaben 2023, Yusuf Gawuna addu’ar samun nasara.