✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

2023: Tsarin watsa sakamakon zabe kai tsaye ta intanet na nan daram —INEC

Ya kamata al‘umma su yi watsi da jita-jitar.

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da rade-radin da ke cewa ta fasa amfani da sabon tsarinta na amfani da na’urorin Bvas da IRev, wajen watsa sakamakon zabe kai tsaye ta intanet daga rumfunan da aka kada kuri’a.

Shugaban Sashin Wayar da Kai da Watsa Bayanai na hukumar, Festus Okoye ne ya bayyana haka ranar Juma’a a Abuja.

A cewarsa, rahotannin da wasu kafofin yada labarai ke yadawa cewa hukumar za ta ajiye tsare-tsare don tafka magudi a zabukan 2023, ba gaskiya ba ne.

“Hukumar na kara tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa za ta watsa sakamakon zabe tun daga rumfunan da aka jefa kuri’a, kamar yadda aka gani a zabukan gwamnonin jihohin Ekiti da Osun.

“Sannan kamar yadda aka gani, bayan wadannan jihohin ma, da tsarin aka yi amfani a zabukan cike gurbi na mazabu 103, da aka yi.

“Kuma sakamakon har yanzu yana nan a shafin hukumar idan kuka duba.”

Kazalika, ya ce ya kamata al‘umma su yi watsi da jita-jitar, domin ba gudu ba ja da baya kan amfani da sabbin tsare-tsaren a dukkanin zabukan 2023 masu karatowa.