✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘A daki daya muke kwana da Sarkin Kano Sanusi’

Har yanzu muna nan kamar yadda muke a baya.

Sarkin Bichi, Alhaji Nasiru Ado Bayero, ya ce sun kasance aminan juna da Sarkin Kano na 14, Muhammadu Sanusi II tun tale-tale.

Ana iya tuna cewa, tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabi’u Musa Kwankwaso ne ya nada Sanusi wanda ke zaman tsohon Gwamnan Babban Bankin Najeriya, a matsayin Sarkin Kano na 14 bayan rasuwar marigayi Alhaji Ado Bayero.

Biyo bayan rarraba masarautar Kano gida hudu, Gwamnan Jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya tumbuke rawanin Sanusi a bara, kuma ya maye gurbinsa da babban yayan Sarkin Bichi, Alhaji Aminu Ado Bayero.

A wata doguwar tattaunawa da Aminiya ta yi a yayin da ake shiryen-shiryen bikin mika masa sanda da kuma auren diyarsa, Sarkin Bichin ya ce akwai kyakkyawar alaka tsakaninsa da korarren Sarkin Kano wacce ana iya daukarta a yi dogon nazari a kanta.

“Tare muka taso, amma ya girme ni da kusan shekaru uku kuma mun kasance aminan juna tun fil azal.

Sarkin Bichin ya ce bayan Sanusi ya dawo fadar Sarkin Kano, a daki daya suka yi rayuwa tun daga kuruciya har suka girma.

“Tare muke karin kumallon safe kuma mun kasance shakikai don babu wasu masu kusanci a duk dangi da ya kai wanda yake tsakani na da shi.

“Aminantakar da ke tsakanina da shi ana iya yin nazari a kanta don ko mahaifanmu tare suka taso.

Dangane da ko an samu sauyi a alakar da ke tsakaninsu, Nasiru Ado ya ce har yanzu akwai kyakkyawar alaka a tsakaninsu kuma sukan tuntubi juna lokaci zuwa lokaci.

“Har yanzu muna nan kamar yadda muke a baya, babu wani sauyi da aka samu dangane da dangartaka ta da shi,” a cewar Sarkin Bichi.

Ku ci gaba da bibiyarmu domin samun cikakkiyar tattaunawar da Aminiya ta yi da Sarkin na Bichi.