✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ni da mahaifiyarmu muna kallo aka zare ran kanina —Dangote

A kan idon Dangote da mahaifiyarsu da ’ya’yan mamacin aka dauki ransa a gadon asibiti.

Attajirin Afirka, Alhaji Aliko Dangote, ya bayyana matukar kaduwarsa kan yadda kaninsa ya rasu a gabansa.

Dangote ya bayyana haka ne a yayin da yake karbar gaisuwar ta’aziyya daga Jagoran Jam’iyyar APC na Kasa, Bola Tinubu.

Ya shaida wa Tinubu a gidansa da ke Kano cewa, rasuwar “Da zafi sosai saboda a gabanmu ya rasu, ni da mahaifiyarmu da kuma ’ya’yansa.”

Dangote ya ce abin da ya fi ban takaici shi ne suna tare da marigayi Sani a gadon jinyarsa, likitoci suka shaida musu cewa cikin sa’a daya ransa zai yi halinsa.

Ya ce ya kadu matuka da ganin yadda ran dan uwansa na fita a asibiti suna kallo.

Kanin nasa, Sani Dangote, wanda shi ne Mataimakin Shugaban Rukunin Kamfanin Dangote ya rasu ne ranar Lahadi a Amurka, inda ake jinyar sa saboda cutar kansa da ya yi fama da ita.

An sallace shi ranar Laraba a Kofar Kudu, Fadar Sarkin Kano, bayan an dawo da gawarsa a safiyar ranar.