✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

A haramta wa Iran shiga Gasar Kofin Duniya —Ukraine

Ukraine na sahun kasashen da suka rasa gurbi a gasar Kofin Duniya.

Gwamnatin Ukraine ta roki Hukumar Kwallon Kafa ta Duniya FIFA da ta haramta wa kasar Iran shiga gasar Kofin Duniya da za ta gudanar a Qatar.

Hukumar Kwallon Kafar Ukraine ce dai ta gabatar da wannan bukata dangane da babbar gasar tamaular da za a fara ranar 21 ga watan Nuwamba a kuma karkare a watan gobe.

Bayan wani zama da kwamitin gudanarwa na Hukumar Kwallon Kafar Ukraine ya gudanar ne kasar ta aike wa FIFA bukatar kunshe a wata sanarwa.

Hukumar ta Ukraine dai ta zargi Iran da bai wa Rasha makamai don taimakawa a mamayar da Moscow ke yi wa kasar.

Rokon ya zo kwanaki kadan bayan da Shugaban kungiyar Shakhtar Donetsk Sergei Palkin ya yi kira da a cire Iran, a kuma bai wa Ukraine din damar maye gurbinta a gasar ta bana.

Ukraine na sahun kasashen da suka rasa gurbi a gasar Kofin Duniyar wadda a wannan karon za ta gudana a Gabas ta Tsakiya.

Ita kuwa Iran wadda ta samu gurbin ta ke fuskantar barazanar gaza zuwa gasar musamman bayan zarge-zargen da ke nuna hannunta a taimakon Rasha.