✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

A Karon Farkon ’Yar Kasar Nijar Ta Lashe Gasar Hikayata

Amira Souley, haifaffiyar garin Maradi Jamhoriyar Nijar, ita ce kuma ta lashe Gasar BBC Hausa ta Rubutun Gajerun Labarai ta Mata, wato Hikayata, ta bana.

Amira Souley, haifaffiyar garin Maradi na Jamhuriyyar Nijar, ita ce ta lashe Gasar BBC Hausa ta Rubutun Gajerun Labarai ta Mata, wato Hikayata, ta bana.

Amira Souley ita ce ’yar Jamhuriyyar Nijar ta farko a tarihi da ta zama gwarzuwar gasar Rubutun Gajerun Labara.

A wannan hirar da Aminiya, ta bayyana irin kalubalen da ta fuskanta a tsawon lokacin da ta kwashe tana rubuta littattafan kagaggun labarai na Hausa har zuwa wannan lokacin da ta samu nasara a gasar Hikayata.