✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Adeleke zai garzaya Kotun Daukaka Kara

Ina kira ga jama'a da su kwantar da hankalinsu.

Gwamnan Jihar Osun, Sanata Ademola Adeleke, ya bayyana cewa zai daukaka kara kan hukuncin da Kotun Sauraron Kararrakin Zaben jihar ta yanke na sauke shi daga mukaminsa a wannan Juma’ar.

Aminiya ta ruwaito Kotun sauraron kararrakin zabe a Jihar Osun tana ayyana Adegboyega Oyetola na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar da aka gudanar a ranar 16 ga watan Yuli.

A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Olawale Rasheed ya fitar, Adeleke ya sha alwashin kalubalantar hukuncin da ya bayyana a matsayin rashin adalci.

Haka kuma, a wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter, Mista Adeleke ya yi kira ga magoya bayansa da su kwantar da hankalinsu, yana mai cewa gaskiya za ta yi halinta a Kotun Daukaka Kara.

Ya ce, “Ina kira ga mutanenmu da su kwantar da hankalinsu.

“Za mu daukaka kara kan hukuncin kuma muna da tabbacin za a yi mana adalci.

“Ina mai tabbatar wa mutanenmu cewa za mu yi duk mai yiwuwa don ci gaba da rike wannan mukami,” in ji Adeleke.