✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Aisha Buhari ta dawo Najeriya bayan wata shida a Dubai

Tun bayan tafiyar Aisha aka yi ta ce-ce-ku-ce kan dalilin tafiyar.

Matar Shugaban Kasa, Aisha Buhari ta dawo Najeriya bayan shafe wata shida a Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE).

Aisha Buhari ta shiga Najeria ne a ranar Laraba, bayan ta bar Najeriya ne kwanaki kadan da bikin daurin auren ’yarta Hanan.

Tafiyar da ta yi ta haifar da ce-ce-ku-ce inda wasu ke zargin rashin tsaro a Fadar Shugaban Kasa ce ta sa ta barin kasar.

Sai dai daga baya hadiman Uwar Gidan Shugaban Kasar sun musanta zargin a matsayin shaci-fadi.

Ko kafin daurin Hanan, Aisha Buhari ta jima Dubai inda aka duba lafiyarta, kafin dawowarsu tare da amaryar gab da bikin.