✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Akeredolu ya lashe zaben Gwamnan Ondo

Akeredolu ya samu nasara a 15 daga cikin kananan hukumomi 18 na jihar Ondo

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta sanar cewa Gwamnan Jihar Ondo Rotimi Akeredolu ne ya lashe zaben gwamna da aka gudanar a ranar Asabar.

Shugaban Jami’ar Ibadan, Farfesa Abel Idowu Olayinka, wanda shi ne Babban Bature zabe na INEC,  yayin bayyana sakamakon zaben a ranar Lahadi ya ce Akeredolu ya samu nasara ne da kuri’a 292,830.

Alkaluman sun nuna Akeredolu da ke neman wa’adin mulki na biyu a jam’iyyar APC ya samu gagarumar rinjaye a 15 daga cikin Kananan Hukumomi 18 na jihar.

Babban abokin hamayarsa, Eyitayo Jegede na jami’ar PDP ya samu kuri’a 195,791 a matsayi na biyu a zaben.

Mataimakin Gwamnan, Agboola Ajayi wanda ya yi takara a karkashin jam’iyyar ZLP shi ne ya zo na uku bayan ya samu kuri’a 69,127.

Nan gaba aka sa ran Farfesa Abel ya sanar da sakamakon zaben na karshe a hukumance.