✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘Akwai masu fada aji da ke neman halasta tabar wiwi a Najeriya’

Ya kamata jama’a su goya mana baya wajen yaki da ta’ammali da tabar wiwi.

Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta ce, akwai wasu masu fada aji da ke kokarin ganin an halasta tabar wiwi a Najeriya.

Shugaban NDLEA, Birgediya Janar Buba Marwa ne ya bayyana haka ne a wajen wani taro da halarta ranar Alhamis a Legas.

Ya ce, “Wasu jiga-jigan Najeriya sun ba da himma wajen neman a halasta tabar wiwi domin ba su damar noma ta.

“Wannan kuwa wata alama ce ta daure wa matasan kasar gindi wajen ci gaba da aikata ba daidai ba,” inji shi.

A cewarsa, maimakon neman a halasta wiwi a kasa, “kamata ya yi jama’a su goya mana baya wajen yaki da ta’ammali da ita.”

Kazalika, ya ce masu safarar miyagun kwayoyi kimanin su 19,000 ne suka fada a komar NDLEA a tsakanin shekaru biyun da suka gabata.

Kazalika, ya ce an samu nasarar hukunta mutum 3,011 daga cikin adadin da aka kama.