✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Alhaji Bako Zuntu ya riga mu gidan gaskiya

Ya rasu ya bar mata biyu da ’ya’ya 26 da jikoki da dama.

Allah Ya yi wa shahararren dan kasuwar nan na Zariya, Alhaji Usman Bako Zuntu rasuwa.

Iyalan mamacin sun ce ya rasu ne da Asubahin Juma’ar nan a Asibitin Al-Madina da ke GRA a Zariya bayan ya yi fama doguwar jinya.

Alhaji Bako Zuntu wanda ta shafe shekaru 84 a doron kasa, ya kasance babban dan kwangila kuma shahararren dilan kayayyakin masarufi a Kamfanin PZ.

An haife shi a garin Zuntu na Karamar Hukumar Kubau da ke Jihar Kaduna, amma ya kasance mazaunin Unguwar Magume da ke Tudun Jakun Zariya duk tsawon rayuwarsa.

Kafin rasuwarsa Alhaji Bako Zuntu, babban manomi ne kuma attajiri da ke amfani da dukiyarsa wajen tallafa wa al’umma.

Ya rasu ya bar mata biyu da ’ya’ya 26 da jikoki da dama.

Wakilinmu ya ruwaito cewa za a yi jana’izarsa a Masallacin Juma’a da ke Makarantar Kimiyya da Fasaha ta Nuhu Bamalli, daura da Kamfanin Buga Takardu na Gaskiya, bayyan an idar da sallar Juma’a.