✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Ambaliyar ruwa ta kashe mutum 57 a Bangladesh da Indiya

Ambaliyar dai ta jefa miliyoyin mutane cikin mawuyacin hali

Sama da mutum miliyan 200 ne ambaliyar ruwa ta shafa a wasu sassan kasashen Bangladesh da Indiya bayan tafka mamakon ruwan sama.

Bayanai daga kasashen biyu sun tabbatar da cewa ambaliyar ta kuma yi ajalin mutum 57.

Rahotanni sun ce, kimanin mutum miliyan daya ne ambaliyar ta shafa a yankin Arewa maso Gabashin Bangladesh.

Wannan ba shi ne karon farko da wannan yankin ya yi fama da irin wannan mummunar ambaliyar ba.

A kasar Indiya kuwa, kimanin kauyuka 100 ne ambaliyar ta mamaye a Zakiganj kamar yadda wani jami’in gwamnati a yankin, Mosharraf Hossain ya bayyana.

A cewar jami’in, “Kawo yanzu kimanin mutum miliyan 200 ne ambaliyar ta jefa cikin mawuyacin hali, kana mutum 10 sun riga mu gidan gaskiya a wannan makon sakamakon ambaliyar.”

Masana sun ce sakamakon sauyin yanayin da ake fuskanta, sassa da dama daga Bangladesh da wasu makwabtansu a Indiya na fuskantar hadarin fama da ambaliya.