✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Amurka na zawarcin hulda ta gaskiya da nahiyar Afirka —Blinken

Ba ma gasa da kowacce kasa wajen neman karbuwa a nahiyar Afirka.

Sakataren Harkokin Wajen Amurka, Antony Blinken da ke ziyara a Afirka ta Kudu, ya ce Amurka na zawarcin hulda ta gaskiya da nahiyar Afirka, sannan kuma ba ta gasa da wata babbar kasa a duniya wajen neman karbuwa a nahiyar ta Afirka.

Tun a Lahadin da ta gabata ce, Mista Blinken ya isa Afrika ta Kudu domin fara ran-gadin kasashen Afirka uku wanda ke zuwa jim kadan da kammala ziyarar da Ministan Harkokin Wajen Rasha Sergei Lavrov ya kai nahiyar.

A yayin gabatar da jawabi ga taron manema labarai a babban birnin Pretoria na kasar Afrika ta Kudu, Sakataren Harkokin Wajen na Amurka ya ce, ba sa kallon nahiyar Afirka a matsayin wani fagen gogayya da manyan kasashen duniya.

A wannan ran-gadin da ya soma a nahiyar Afirka, Mista Blinken ya fara yada zango ne a Afirka ta Kudu, kasar da ke zama jagora a jerin kasashen duniya maso tasowa wadda kuma ta dauki matsayin ’yan ba-ruwanmu a rikicin Rasha da Ukraine.

Afrika ta Kudu dai ta yi kememe, inda ta ki bin sahun kasashen Yammacin Duniya wajen sukar gwamnatin Moscow da ke kaddamar da farmaki a Ukraine.

Mista Blinken din ya kuma sanar da wasu sabbin manufofin Amurka a nahiyar Afirka a wani jawabi da ya yi a jami’ar Pretoria.