Karin dalibai uku daga cikin wadanda aka yi garkuwa da su a makarantar sakandaren Bethel Baptist sun kubuta daga hannun ’yan bindigar.
An ceto karin daliban ne a cikin daji, kwanaki kadan bayan wasu biyu sun kubuta daga hannun masu garkuwar.
- Mutum 1 ya tsere yayin da ’an bindiga suka sace mutum 8 a Neja
- Manyan shari’o’i 5 da aka ‘kwanta’ kansu a Najeriya
Shugaban makarantar, Rabaran Adamu Jangado, ya tabbatar wa wakilinmu ta wayar tarho cewa jami’an tsaro sun gano daliban ne a Daji Kakuma da ke Jihar, suka kuma ceto su a ranar Talata.
Rabaran Adamun, wanda kuma shi ne mai makarantar bai yi wa wakilin namu karin bayani ba.
Kakakin ’yan sanda a Jihar Kaduna, ASP Mohammed Jalige, ya tabbatar da kubutar da karin daliban, amma ya ce hukumar makarantar ba ta sanar da su a hukumance ba.
A ranar 5 ga watan Yuli, 2021 ne ’yan bindiga suka kutsa makarantar sakandaren Bethel Baptist da ke kan hanyar Kaduna zuwa Kachi, suka sace dalibai 121.
A kwanakin bayan masu garkuwar sun sako 28 daga cikin yaran bayan iyayensu sun biya kudin fansa.
Kawo yanzu dai mutum 80 daga cikin yaran ne ke hannun masu garkuwar.