✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An daure matar da aka kama da miyagun kwayoyi watanni 30 a gidan kaso

Kotu ta yanke wa matar hukuncin ne ba tare da wani zabi ba na biyan tara

Wata Babbar Kotun Tarayya mai zamanta a Kaduna, ta yanke wa wata mata Helen Carlos hukuncin zama kurkuku na wata 30 bayan da aka kama ta da miyagun kwayoyi.

Kotun karkashin jagorancin Mai Shari’a Mohammed Garba, ta yanke hukuncin ne bayan da matar ta amsa laifin da aka tuhume ta da shi.

Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) ce ta gurfanar da matar a kotu don ta fuskanci hukunci daidai da laifin da ta aikata.

Kotu ta yanke wa matar hukuncin ne ba tare da wani zabi ba na biyan tara.

Kuma an yake mata zaman kaso na watanni 30 din ne duba da ba a taba kama ta da wani lafi a kotu ba sai a wannan karon.

Kotun ta gargadi matar kan ta guji jefa kanta cikin ta’ammali da miyagun kwayoyi idan ta kammala zaman kaso ta fito.

Tun farko, lauyan NDLEA, T.J. Atserhegh, ya shaida wa kotun cewa a ranar 14 ga Satumba ce jami’an hukumar suka damke Carlos a babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja.

Ya ce an kama ta ne dauke da kunshin tabar wiwi da kuma kwayar Taramol wanda hakan ya saba wa dokar kasa.

(NAN)