✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An farke cikin mai juna biyu an sace dan tayin

Wasu da ba a san ko su wane ne ba sun kashe mai ma juna biyu, suka farke cikinta, suka dauke dan tayin

Wasu da ba a san ko su wane ne ba sun kashe wata mai ma juna biyu, suka farke cikinta sannan suka dauke dan tayin da ke ciki.

Rahotanni sun ce an tsinci gawar matar mai juna biyu ne a yashe a kan wani juji a Rukunin Gidajen Alkalai da ke Makurdi, babban birnin Jihar Binuwai.

Aminiya ta gano cewa tsinci gawar mai juna biyun ce kwana kadan bayan ’yan sanda sun tsinci gawar wata dalibar jami’a a unguwar.

Wani ganau da ya ce a boye sunansa ya bayyana cewa mai juna biyun da aka tsinci gawarta an farke cikinta an tafi da dan tayinta, wata mai tabin hankali ce da ke yawo a yankin.

Kakakin Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Binuwai, SP Catherine Anene, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta bayyana cewa an dauke gawar zuwa mutuwari.