✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An ga watan Shawwal a Nijar

Laraba take sallah a Jamhuriyyar Nijar.

Gwamnatin Nijar ta sanar da ganin watan Shawwal, wanda ya kawo karshen watan azumin Ramadan a kasar.

Firaiminista Ouhoumoudou Mahamadou ne ya tabbatar da ganin jaririn watan a yammacin Talata kamar yadda sashen Hausa na BBC ya ruwaito.

Sanarwar ta ce an ga watan ne a cikin yankunan Nijar uku.

Wannan na zuwa bayan Najeriya, makwabciyar Nijar ta sanar da cewa ba a ga watan ba tare da ayyana Alhamis a matsayin ranar Sallah.

Haka kuma, wannan na zuwa ne yayin da wasu kasashen musulmi na duniya suka sanar da rashin ganin watan a yau Talata.

Daga cikin kasashen da akwai Indonesia, Jordan, Malaysia, Qatar, Saudiyya, Turkiyya, da Hadaddiyar Daular Larabawa.