✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An gano karin gawarwaki 13 na mutanen da hatsarin kwalekwalen Bagwai ya ci

Kawo yanzu mutum 42 suka rasu a hatsarin kwalekwalen da ya ritsa da daliban Islamiyya a harsu ta zuwa taron Mauludi

Yawan mutanen da suka rasu a hatsarin kwalekwalen da ya ritsa da matafiya a Karamar Hukumar Bagwai ta Jihar Kano ya karu zuwa 49.

Adadin ya kau ne bayan an gano karin gawarwaki 13 a hatsarin da ya ritsa da mutanen, cikinsu har da daliban Islamiyya da ke hanyarsu ta zuwa taron Mauludi.

Majiyoyi sun ce mutum 49 ne a kan kwalekwalen a lokacin da ya kife da fasinjojin, yawancin su daliban makarantar Madinatul Islamiyya da ke kauyen Badau a karamar hukumar.

Da farko bayan hatsarin, an ceto mutum bakawai daga cikin fasinjojin da ransu, aka kuma gano gawarwaki 29, kafin karin gawarwaki 13 da aka gano daga bisani.

Lamarin ya ritsa da matafiyan ne a kan hanyarsu ta zuwa halartar wani taron Mauludi da reshen makarantar da ke garin Bagwai ya shira.

Gwamna Abdullahi Ganduje na Jihar Kano ya yi zargin cewa kayan da kwalekwalen ya dauka fiye da kima ne ya haddasa hatsarin, sannan ya kafa kwamitin bincike domin gano ainihin abin da ya faru.

Tuni dai gwamnatin jihar ta haramta amfani da kwalekwalen haya a yankin Bagwai, ta kuma bayar da bas-bas guda biyu domin a rika amfani da su wajen jigilar mutane tsakanin garin Bagwai da kauyen Badau.

Ta kuma bayar da tallafin Naira miliyan shida da buhu 120 na shinkafa da masara da sukari 60 ga iyalan mamatan.