✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An jefe ni har sau biyu lokacin kamfe a Katsina – Peter Obi

Sai dai dan takarar ya tsira ba tare da ya ji rauni ba

Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar LP, Peter Obi, ya ce wasu bata-gari sun jefe shi har sau biyu bayan kammala yakin nema zabensa a Katsina.

Cikin wata sanarwa da kakakinsa, Diran Onifade ya fitar ranar Talata, ya ce jifan abin Allah-wadai ne.

“Dan takararmu ya jagoranci tattaunawa da mata a jihar, daga na ya wuce taron yakin neman zaben da aka gudanar a filin wasa na Muhammad Dikko.

“Sai dai a kan hanyarsa ta zuwa filin jirgi ne bata-gari suka hau jifan motar da yake ciki, har suka yi mata rotse.

“Mun zaci shikenan amma da muka yi gaba sai da aka sake samun wasu suka jefe motocinmu kan mu isa filin, Allah ya taimaka babu wanda ya samu rauni,” in ji Onifade.

A cewarsa, jifa na biyun ne ya sa suka fahimci shiri ne na ’yan siyasar da a baya suka yi ikirarin yankin Arewa maso Yammacin Najeriya nasu ne ba na Obi ba, amma zuwansa jihar ya nuna akasin haka.

Sai dai Peter Obj ya yaba wa Katsinawan kan yadda suka yi dafifin tarar shi, inda ya bukaci jami’an tsaro su bankado batagarin don hukunta su.