Akalla mutum uku na can kwance a asibiti bayan wasu ’yan daba sun kai wa magoya bayan dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar hari a jihar Ribas.
Rahotanni sun ce maharan sun harbi Ko’odinetan kamfen din Atiku na Karamar Hukumar Omuma, Nnamdi Nwogu da kuma Udochukwu Nwakpala, da wasu mutum uku.
- ASUU ta fara taron gaggawa kan rikicin albashi
- Sojoji sun harbe ’yan ta’adda suna tsaka da girbi a gonar manoma a Zamfara
An dai kai musu harin ne lokacin da suke lika fastocin dan takarar a yankin Eberi na Karamar Hukumar a ranar Lahadi.
Bayanai sun nuna mutanen sun sami raunuka a saran da aka yi musu da adduna a jikinsu, lokacin da matasan kimanin su 30 suka far musu.
Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar, SP Grace Iringe-Koko, har yanzu bai magantu ba a kan batun.