✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kama masu garkuwa da mutane 9 a Ekiti

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta sanar da kama wasu da take zargin masu garkuwa da mutane ne su tara a Jihar Ekiti. Mutanen da aka…

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta sanar da kama wasu da take zargin masu garkuwa da mutane ne su tara a Jihar Ekiti.

Mutanen da aka kama a garin Ago Adulojh da ke Ado Ekiti, sun shiga hannu ne a kokarin rundunar na kakkabe yan ta’adda daga cikinta.

Kakakin rundunar, ASP Sunday Abutu ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin.

A cewarsa, sun sami wannan masara ce a sakamakon wasu bayanan sirri da suka samu kam yadda wadanda ake zargin suka yi wa dajin Agon dirar mikiya.

An kama su ne a dajin wanda tun a baya ke da tarihin zama mafakar masu aikata laifuka.

Kwamishinan ’yan sandan jihar CP Morenkeji Adesina ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa ba zai yi kasa a gwiwa ba wajen kama bata gari da daukar mataki kansu.