✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kama Sarakuna biyu kan harin tashar jirgin kasan Edo

An samu nasarar kubutar da mutum biyu da suka rage a hannun masu garkuwa da mutanen.

Gwamnatin Jihar Edo, ta ce ta kama sarakuna guda biyu tare da wasu mutum biyar wadanda ake zargi da hannu a garkuwa da fasinjoji 20 a harin da aka kai tashar jirgin kasa a jihar ranar 7 ga watan Janairu.

Kwamishinan Sadarwa da Wayar da Kai a jihar, Chris Nehikhare, shi ya bayyana hakan jiya Laraba a Benin, yayin zantawa da manema labarai jim kadan bayan fitowa daga taron Majalisar Zartaswa.

Ya ce jami’an tsaro sun samu nasarar kubutar da mutum biyu da suka rage a hannun masu garkuwa da mutanen.

“Mun kuma samu nasarar cafke mutane bakwai da a ake zargi ciki hara da wasu sarakunan kauye biyu.”

A ranar 7 ga watan Janairu ne, wasu da ake zargin ’yan bindiga suka kai hari tashar jirgin kasa a jihar tare da sace mutum 20.