✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kama shi yana bayan gida a masallaci a Kaduna

An kama dayansu yana bayan gida a masallaci saboda a ba shi N20,000

Dubun wasu mutane da suka hada baki dayansu ya yi bayan gida a masallaci rana tsaka a cikin watan Ramadan domin a ba shi kudi ta cika a Jihar Kaduna.

Wata kotun Musulunci a jihar ta ba da umarnin tsare mutum biyun da aka kama kan yin wannan aika-aika a harabar masallacin da ke layin Alkalawa a unguwar Tudun Wada da ke garin Kaduna.

Dubun wadanda ake zargi ta cika ne har mutanen gari suka kama su bayan daya daga cikinsu ya yi bayan gida a masallacin da taimakon dayan abokin cin mushensa.

Bayan al’ummar unguwar sun cafke su ne suka mika su a hannun ’yan sanda kafin a gurfanar da su a gaban kotun ne kan zargin neman tayar da zaune tsaye.

Kotun da ke zamanta a Magajin Gari a Karamar Hukumar Kaduna ta Arewa ta bayar da umarnin ne a ranar Alhamis.

Da yake jawabi a gaban kotun, dan dansa mai gabatar da kara, Insfekta Ibrahim Shuaibu, ya ce an mika mutanen ofishin ’yan sanda na unguwar Tudun Wada ne a ranar 11 ga watan Afrilu, 2022 bayan an kama su.

Ya ce an kama daya daga cikin mutanen ne dumu-dumu yana bayan gida a masallacin, saboda dayan ya yi alkawarin zai ba shi N20,000 idan har ya yi kashi a masallacin.

Wadanda ake zargin dai sun musanta aikata laifin da ake tuhumar su da aikata wa.

Alkalin kotun, Malam Rilwanu Kyaudai, ya ba da umarnin a ci gaba da tsare su, sannan ya dage sauraron shari’ar zuwa ranar 28 ga watan Afrilu.