✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kashe mutane 645 cikin watanni shida a Kaduna

An kashe kashi daya bisa uku a Kudancin Kaduna.

Gwamnatin Jihar Kaduna ta ce hare-haren masu dauke da makamai sun kashe mutane 645 a jihar cikin watanni shida daga watan Janairu zuwa Yuni wannan shekara ta 2022.

Hakan na kunshe ne cikin wani rahoton tsaro kan tashe tashen hankula da gwamnatin jihar ta fitar ranar Juma’a.

Rahoton ya bayyana cewa, an kashe adadin wadannan mutane ne a hare-haren ta’addanci da fadan kabilanci da kuma na ‘yan fashin daji.

Kwamishinan Tsaro da Harkokin Cikin Gida na jihar, Samuel Aruwan, a sanarwar da ya fitar ya ce kusan kashi daya bisa uku na wadanda aka kashe (234) an kashe su ne a Kudancin Kaduna.

“A cikin watanni shida na farkon shekarar 2022, mutane 645 ne suka rasa rayukansu a irin wannan yanayi a fadin jihar; 234 daga cikin wadannan sun faru ne a yankin Kudancin Kaduna,” in ji Mista Aruwan a taron gabatar da rahotannin zaman lafiya a tsakanin addinai.