✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kashe wani mutum a rikicin APC da PDP a Jigawa

Mutum daya ya rasa ransa sakamakon arangamar da magoya bayan jam'iyyun biyu suka yi da juna.

Akalla mutum daya ne ya rasa ransa, wasu biyar kuma suka jikkata bayan wani rikici da ya barke tsakanin magoya bayan jam’iyyar PDP da na APC a Jihar Jigawa.

Lamarin ya faru ne a lokacin da dan takarar gwamnan jihar na PDP, Mustafa Sule Lamido, ya gudanar da yakin neman zabensa a Karamar Hukumar Maigatari ranar Juma’a.

Rahotanni sun ce bayan isarsu Sakatariyar Jam’iyyar APC, rikici ya barke tsakaninsu da magoya bayan APC.

A cewar sanarwar da ’yan sandan suka fitar, magoya bayan PDP ne suka kai wa wani matashi mai suna Abdullahi Isiyaku, mai shekara 37 da ke zaune a garin Gangare a Maigatari, hari.

An garzaya da shi Babban Asibitin Gumel domin yi masa magani amma daga baya ya mutu sakamakon raunin da ya samu.”

Sanarwar ta kara da cewa, ana gudanar da bincike a sashen binciken manyan laifuka na jihar (SCID) da ke Dutse.

Kakakin rundunar , DSP Lawan Shiisu Adam, ya ce ’yan sanda na bincike domin ganin an gurfanar da wadanda suka aikata laifin a gaban kuliya.

Lamarin da ya haifar da fargaba da tsoro a zukatan mazauna yankin.