✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An koma karatu a Jami’ar ABU

Kimanin wata uku tun bayan janye yajin aikin Kungiyar Malaman Jami'a (ASUU)

Harkokin koyo ka koyarwa sun dawo gadan-gadan A Jami’ar Ahmadu Bello (ABU) ta Zariya a ranar Talata.

Daliban jami’ar sun koma aji a wannan satin ne kamar yadda  jaddawalin shekarar karatu na 2021/2022 da hukumar makarantar ta amince da shi.

Hakan kuwa na zuwa ne kimanin wata uku tun bayan janye yajin aikin Kungiyar Malaman Jami’a (ASUU) a watan Oktoba, 2022.

Sai dai kuma bincike ya nuna cewa kalilan daga cikin dalibai ne suka dawo makarantar suka fara daukar darussa.

A wani zagayen gani da ido da mahukuntan jami’ar suka gudanar, karkashin jagorancin Shugaban Jami’ar, Farfesa Kabiru Bala, ya bayyana rashin jin dadi bisa karancin dawowar dalibai.

Su ma wasu jami’an jami’ar da suka zagaya sun nuna rashin jin dadinsu bisa rashin dawowar daliban duk kuwa da sanin cewa an fara karatu ka’ina-da-na’in.

Koda yake babu tabbacin ko karancin dawowar daliban na da nasaba da hutun bukukuwan karshen shekara da aka kammala a ranar Litinin.

Duk da haka, a lokacin da wakilinmu ya ziyarci sashen nazarin aikin lauya na jami’ar da ke Kongo, ya tarar dalibai da yawa sun dawo.