✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kona rugar Fulani kan garkuwa da mutane

Mahara sun kona wata rugar Fulani bisa zargin garkuwa da mutane a Jihar Ogun.

Mahara sun kona wata rugar Fulani bisa zargin garkuwa da mutane a yankin Iraye da ke Shagamu a Jihar Ogun.

Mazauna yankin sun kai wa rugar hari, inda suka kona gidaje, suka jikkata mutum daya wasu kuma suka tsere zuwa inda ba a sani ba.

Wakilinmu ya gano cewa al’ummar Iraye na zargin Fulani da hannu a satar mutane da ake yi a yankin.

Wani bidiyo ya fita wanda ke zargin wasu Fulani da hannu a sace wani manomi; Bidiyon ya ce hatsaniyar ta barke tsakanin bangarorin ne a yayin yunkurin kubutar da wadanda ake zargin an sace.

Shugaban Kungiyar Miyetti Allah ta MACBAN, reshen Jihar Ogun, Abdulmumin Ibrahim, ya ce, “An kira ni da misalin karfe 9 na dare cewa an kona rugar Fulani a Sagamu saboda zargin satar mutane.

“Mutanen rugar sun tsere amma akwai mutum biyu da ba a gani ba. Ba za a iya cewa suna raye ko sun mutu ba; Amma zan tuntube ka idan na samu cikakken bayani,” kamar yadda ya bayyana.

Kakakin ’yan sandan Jihar Ogun, Abimbola Oyeyemi ya ce, “Lamarin ya faru ne a Iraye inda ake zargin Fulani makiyaya da yin garkuwa da wani manomi a gonarsa.

“Shi ne mutanen suka je suka kona rugar; An ji wa bafulatani daya rauni kuma an kai shi asibiti ana kula da shi,” inji shi.