✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kubutar da ma’aikatan Jami’ar Abuja daga hannun masu garkuwa da su

An kubutar da su ne da taimakon 'yan bangar yankin Abaji.

Jami’an ’yan sanda a yankin Babban Birnin Tarayya Abuja sun sami nasarar kubutar da ma’aikatan da ‘yan bindiga suka sace a rukunin gidajen ma’aikatan Jami’ar Abuja.

Rahotanni sun ce an kubutar da mutanen ne tare da hadin guiwar ’yan bangar yankin Abaji, kan babbar hanyar Abuja zuwa Lokoja.

A ranar Talata ne wasu gungun ’yan bindiga suka kai hari jami’ar inda suka yi awon gaba da wasu ma’aikatanta.

Wani ma’aikacin jami’ar ne ya tabbatar da kubutar da mutanen ranar Laraba.

Ya ce an kubutar da su a yammacin ranar Talata da taimakon ’yan sanda da ’yan banga, kuma yanzu haka suna ofishin ’yan sandan na Abaji.

Tun bayan aukuwar lamarin, jami’an tsaro suka ce an samar da babura kusan 13 da kuma motoci ga sojoji domin shiga dajin da ke kusa da makarantar domin neman wadanda aka sace.