✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kwace na’urar BVAS guda 8 —INEC

Shugaban INEC ya koka da ceaw mahara sun mayar da hanklai wajen kwace na'urorin BVAS

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta ce ’yan daba sun tarwatsa wuraren zabe tare da da sace na’urar tantance masu zabe (BVAS) guda takwas a jihohin Delta da Katsina.

Shugaban INEC na kasa, Farfesa Mahmood Yakubu, ya bayyana cewa ’yan daba sun kwace na’urar BVAS guda shida a wani hari da suka kai rumfar zabe a Karamar Hukumar Safana a Jihar Katsina, inda suka yi.

An kai makamancin harin a Karamar Hukumar Oshimili a Jihar Delta, inda sauka yi awon gaba da na’urar BVAS guda biyu.

Ta sanar da haka ne a ranar Asabar yayin da yake jawabi game da zaben Shugaban Kasa da na ’yan Majalisar Tarayya da ke gudana.

Yakubu ya koka kan cewa, bayyane yake bata-garin sun maida hankalinsu ne kan na’urorin BVAS da ake amfani da su a wannan zabe.

Ya ce, ”Muna ba da tabbacin za mu ci gaba da yin abin da shi ne daidai, shi ya sa muka zabi yi wa ’yan kasa bayani a daidai wannan gabar, kuma za mu ci gaba da yin haka.

Ya ce hakki ne da ya rataya a wuyan INEC tabbatar da sahihin zabe a kasa.