✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An nada Sanata Ahmad Lawan sarauta a kasar Ibo

An yi wa Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan nadin sarauta a kasar Ibo, inda ya yi kira ga jama’ar sassan Najeriya su zauna lafiya da…

An yi wa Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan nadin sarauta a kasar Ibo, inda ya yi kira ga jama’ar sassan Najeriya su zauna lafiya da junansu.

An nada Sanata Ahmad Lawan mukamin Babban Cif mai matsayin ‘Nwannedinamba I’ na Igbere, wanda Masarautar Yabi ta Igbere karkashin jagorancin Ndi Eze ta yi a ranar Lahadi a Igbere Ebiri, Jihar Abiya.

Daga cikin wadanda suka halarci nadin sarautar akwai Mai Tsawatarwar Majalisar Dattawa, Sanata Orji Uzor Kalu, Mataimakinsa, Aliyu Sabi Abdullahi, Mataimakin Shugaban Marasa Rinjaye Sahabi Ya’u, Sanata Sani Musa da kuma Shugaban Ma’aikatan Majalisa, Babagana Aji.

Ahmad Lawan yayin da yake karbar shaidar nadin sarautar
Ahmad Lawan da tawagar da suka raka shi amsar nadin sarautar