✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An nada Sarkin Kano a matsayin Uban Jami’ar Kalaba

Sarkin ya gode wa Gwamnatin tarayya kan martaba shi da aka yi.

Gwamnatin Tarayya ta amince da nadin Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, a matsayin Uban Jami’ar Kalaba, da ke Jihar Kuros Riba.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin Jami’ar, Matthew Luther Agwai, ya fitar a ranar Laraba.

Ya ce hukumar gudanarwar Jami’ar na farin ciki da nadin Sarkin a matsayin Uban Jami’ar.

Agwai, ya ce gogewar Sarkin zai kawo ci gaba mai tarin yawa ga Jami’ar.

A nasa jawabin, Sarkin Aminu Ado Bayero, ya gode wa Gwamnatin Tarayya kan yadda ta martaba shi na nada shi a matsayin.

Ya ce, “Muna sane da yadda abubuwa suke a Jami’ar Kalaba a Jihar Kuros Riba, za mu tabbatar da samun ingantaccen ci gaba ta fagen ilimi.”

Kazalika, Sarkin ya bukaci hadin kai da goyon baya daga masarautar Kano tare da al’ummar Jami’ar don a kai ga gaci.

Har wa yau, ya bukaci hadin kan dukkanin masu ruwa da tsaki da kuma Hukumar Gudanarwar Jami’ar, don tabbatar da ci gaba mai dorewa.