✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An sake dage zaben kananan hukumomin Kaduna

KADSIECOM ta dage zaben ranar 14 ga watan Agusta da sati uku.

Hukumar Zabe ta Jihar Kaduna (KADSIECOM) ta sanar da sake dage ranar gudanar da zaben kananan hukumomi zuwa ranar 4 ga Satumba, 2021.

Shugabar Hukumar, Saratu Dikko ce ta sanar da hakan a lokacin da take ganawa da masu ruwa da tsaki a ranar Litinin.

Kafin dagewar ta ranar Litinin, KADSIECOM ta sanar cewa za ta gudanar da zaben kananan hukumomin ne a ranar 14 ga watan Agusta, 2021.

Karin labarin na tafe.