✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An yi garkuwa da mutum 18 a Kaduna

Mutanen yankin sun shiga firgici bayan ’yan bindigar sun sace mutum 18.

Akalla mutum 18 ne ake fargabar ’yan bindiga sun yi garkuwa da su a unguwar Keke da ke Karamar Hukumar Chikun ta Jihar Kaduna.

An rawaito cewa ’yan bindigar sun shiga unguwar ce da misalin karfe 12 na dare, suna harbi a iska.

Wani wanda ya gane wa idonsa, ya bayyana cewa ’yan bindiga masu yawan gaske ne suka shiga unguwar, sannan suka sace mutum 18.

Wakilinmu ya bayyana cewa tuni jami’an ’yan sanda suka isa yankin don tsananta bincike kan faruwar lamarin.

Sai dai har yanzu babu wani tabbacin faruwar lamarin daga bangaren rundunar ’yan sandan jihar.

Cikakken bayani na tafe…