’Yan bindiga sun yi garkuwa da suruka da kuma dan uwan Kwamishinan Matasa da Bunkasa Wasanni a Jihar Sakkwato, Bashir Gorau.
Kwamishinan ya sanar cewa, “Da misalin karfe 12:45 na safe ne ’yan bindiga suka kai hari gidanmu da ke Garin Gorau, Karamar Hukumar Goronyo suka tafi da matar babban yayanmu Alhaji Lawali Gorau da wani dan uwanmu Hassan Manya.
- Jiragen sama ke kai wa ’yan bindiga makamai —Fadar Shugaban Kasa
- Abin da mahaifina ya fada min a hannun ’yan bindiga —Dalibar da aka sako
“Allah Ya kiyaye ya kuma dawo mana da su lafiya, Amin; Muna bukatar addu’o’nku,” inji shi.
Ya shaida wa wakilinmu a waya cewa da zuwan maharan suka fara harbi babu kakkautawa.
Sai dai ya ce surukar tasa da dan uwan nasa kadai ne ’yan bindigar suka yi garkuwa da su a kauyen.
“Har yanzu muna jiran kiransu don sanin bukatunsu,” inji Kwamishinan.