✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An yi shari’ar ’yan ta’adda 1000 cikin watanni 18 —Malami

An yanke wa mutum 312 hukunci cikin watanni 18.

Ministan Shari’a, Abubakar Malami, ya ce an yi shari’ar ’yan ta’adda 1,000 da ke fuskantar tuhume-tuhume a kotuna daban-daban cikin watanni 18 da suka gabata.

Ministan ya bayyana haka ne a zantawarsa da ’yan jarida a Fadar Shugaban Kasa ranar Alhamis.

Da yake bayyana ayyukan ma’aikatarsa da irin nasarorin da ta samu ta fuskar gabatar da kara musamman wadanda ake zargi da aikata ta’addanci, Malami ya ce cikin wadannan adadi, 312 na wadanda ta gabatar a gaban alkali, an yanke musu hukunci a tsakanin wadannan watanni.

Cikin wadanda ma’aikatar ta gurfanar, an yanke wa 45 hukunci a kararraki masu sarkakiya a bangaren harkokin teku, da laifukan da suka shafi samar da wutar lantarki na kwamitin kar-ta-kwana.

Malami ya ce ma’aikatar ta gudanar da ayyukan ne tare da hadin gwiwar rassanta 13 da ke fadin kasar, da kuma bangaren da ke kula da shari’ar muggan laifuka na CCG.

Kazalika, ya ce ma’aikatar za ta ci gaba aiki kafada-da-kafada da Babbar Kotu Tarayya da Hukumar Bayar da Taimakon Lauyoyi ta kasa, da kuma Ma’aikatar Tsaro.