✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An zaɓi Musulmi shugaban gwamnatin Scotland

A shekarar 2011 aka fara zaɓensa ɗan Majalisar Dokokin Sikotland.

A karo na farko, an zaɓi Musulmi ya zama shugaban gwamnatin yankin Scotland dake cikin ƙasar Birtaniya.

Jam’iyyar SNP mai mulki ce ta zaɓi Humza Yousaf a matsayin shugabanta kuma shugaban gwamnatin yankin.

Wannan ne dai karo na farko da wata babbar jam’iyya a Haɗaɗɗiyar Daular Burtaniya da Arewacin Ireland ta zaɓi musulmi a matsayin shugaba.

A ranar Talata ne kuma ake sa ran Humza Yousaf mai shekaru 37 zai ɗare kujerar shugabancin Scotland.

Mahaifin Mista Yousaf dai ya yi hijira daga Pakistan zuwa Scotland ne a shekarun 1960 yayin da mahaifiyarsa kuma ƴar asalin Pakistan ce da aka haife ta a Kenya.

A shekarar 2011 aka fara zaɓensa ɗan Majalisar Dokokin Scotland.

Kafin nasara a zaɓen, shugaban gwamnatin ya riƙe muƙamin minista a ma’aikatun sufuri, shari’a, da lafiya.

Bayan da ya yi nasara a zaɓen ya sha alwashin jagorantar Scotland a gwagwarmayar samun ƴancin kai daga Burtaniya.