✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Asarar da aka tafka a sabon rikicin Adamawa

Rikicin ya faro ne a almurun ranar Litinin inda wasu bata-bari suka rika cinna wa gidaje da shaguna wuta a garin Lafiya.

An kona gidaje da shaguna da wasu kadarori na miliyoin Naira a sabon rikicin al’ummomin Waja da Lunguda da ke Karamar Hukumar Lafiya-Lamurde a Jihar Adamawa.

Rikicin ya faro ne a almurun ranar Litinin inda wasu bata-bari suka rika cinna wa gidaje da shaguna wuta a garin Lafiya.

Kakakin ’yan sandan Jihar Adamawa, SP Suleiman Yahaya Nguroje, ya ce ba a samu asarar rai rikicin ba, amma bata-garin sun kona gidaje hudu da shaguna 11.

A cewarsa, Kwamishinan rundunar, S.K. Akande, ya ziarci yankin da aka samu hasaniyar domin tabbaar da doka da oda a ranar.

A cewarsa, rundunar za ta sana kafar wando da duk wanda aka kama da alaka da tashin-tashinar.