✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

ASUU ta yi barazanar maka DSS a gaban kotu

ASUU ta ce abin takaici ne yadda DSS ta koma cin zarafin jama'a.

Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Kasa (ASUU) ta sha alwashin maka Hukumar Tsaron Farin Kaya ta DSS a kotu bisa zargin cin zarafin jami’inta na shiyyar Kano, Farfesa Abdulkadir Mohammed.

Shugaban kungiyar reshen Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya, Farfesa Rabiu Nasiru ne ya sanar da haka a ganawar sa da manema labarai a Zariya ranar Juma’a.

Nasiru ya ce al’amarin ya auku ne a ranar 18 ga watan Augustan 2021 wanda ya ce harkan ya saba wa yancin dan Adam.

A cewarsa, abin takaici ne a ce hukamar da aka samar da ita tun zamanin turawan mulkin mallaka a shekarar 1948, domin ba da tsaron cikin gida amma sai ta rikide da koma tana cin zarafin al’umma.

Farfesa Rabiu ya ce wannan ba shi ne karon farko da hukumar ke cin zarafin masu mutunci ba domin a baya ma ta kama tare da tozartar da editan mujallar Newswatch a shekarar 1988, da kuma editan jaridan mujallar Tell.

Ya kuma yi zargin cewa hukumar ta kasance ta ke gudanar da aikinta na cin zarafin ’yan kasa a maimakon kare mutuncin su.

Shugaban na ASUU ya ce a kan haka suke kira ga hukumar ’yan sanda ta kasa da lallai ne ta gano wadanda suka aikata haka tare da ladaftar da su tare da tabbatar da an gyara motarsu da aka fasa, in bah aka ba kuma su garzaya kotu.

Ya kuma yi kira ga ’yan majalisa na kasa da su sake duba kundin dokar da ya samar da hukumar domin yi mata kwaskwarima.