✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

ASUU za ta sake komawa yajin aiki

ASUU ta ba gwamnati wa’adin Talata 31 ga Agusta, 2021.

Kungiyar Malaman Jami’a ta Najeriya (ASUU) ta bayyana cewa a shirye take ta shiga wani sabon yajin aiki kan abin da ta kira gazawar gwamnati wajen cika alkawuran da aka cim-ma da ita.

Kungiyar ta ce ta bai wa gwamnati wa’adin ranar Talata 31 ga Agusta, 2021, ta tuntube ta, ko kuma ta tsunduma yajin aiki.

Shugaban ASUU, Farfesa Emmanuel Osodeke ne ya bayyana hakan a tattaunawarsa da manema labarai a ranar Lahadi.

A cewar Farfesa Osodeke, a yanzu gwamnati ta daina sauraron su domin kuwa ta ma daina amsa kiran wayarsu.

A watan Maris din 2020, ASUU ta tsunduma yajin aiki bayan rashin jituwa da ta samu da gwamnati kan kudaden da take bai wa jami’o’i da wasu tsare-tsaren albashi da alawus-alawus.

An janye yajin aikin ne bayan gwamnatin da ASUU sun sanya hannu kan wata yarjejeniya domin biya wa kungiyar bukatunta, abin da ya ba da damar yanje yakin aikin a ranar 24 ga Disamba, 2020.

Sai dai rahotanni sun bayyana cewa, har yanzu gwamnatinn ba ta gama cika bangarenta ba a yarjejeniyar da ta kulla da kungiyar malaman jami’ar.