Dan takarar shugaban kasa na PDP, Atiku Abubakar da Shugaban jam’iyyar, Iyorchia Ayu, sun jagoranci jiga-jigan jam’iyyar gudanar da zanga-zanga neman a soke zaben shugaban kasa da aka gudanar.
Masu zanga-zangar da suka sa bakaken kaya sun fara taruwa ne a ofishin jam’iyyar, daga nan suka fara tattaki zuwa Hedikwatar Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) da ke Maitama a Abuja.
- Kotu ta aike da matasan da suka kone ofishin INEC kurkuku
- Mun gano ’yan siyasar Kano da ke shirin dauko bakin ’yan daba —’Yan sanda
Abiye Sekibo, Dino Melaye, da Uche Secondus na daga cikin jiga-jigan jam’iyyar PDP da aka hanga a wajen zanga-zangar.
INEC dai ta ayyana Bola Ahmed Tinubu na Jam’iyyar APC mai mulki a matsayin zababben shugaban kasa.
Sai Atiku Abubakar na PDP a matsayi na biyu, Peter Obi na LP a matsayi na uku, sai Rabiu Musa Kwankwaso na NNPP ya kare a na hudu.
Duk da matsin lamba da hukumar INEC ke sha da neman soke zaben, Farfesa Mahmood Yakubu, shugaban hukumar, ya tabbatar da cewar zaben da aka gudanar sahihi ne.