✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Atiku ya nada Dino Melaye kakakin yakin neman zabensa

Kafin nadin nada, Melaye ya kasance tsohon Sanata daga Jihar Kogi.

Dan Takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya nada Sanata Dino Melaye a matsayin kakakin yakin neman zabensa.

A wata sanarwa da mai bai wa Atikun shawara kan harkokin yada labarai, Paul Ibe, ya sanya wa hannu ranar Alhamis, ya bayyana sunan Melaye tare da Dokta Daniel Bwala a matsayin wadanda ya bai wa sabbin mukamai.

“Nade-naden nasu su biyu zai fara aiki nan take,” inji Ibe a cikin sanarwar.

Melaye ya kasance dan majalisar dattawa ta takwas, wanda ya wakilci mazabar Kogi ta Yamma.

Ya fito daga Ayetoro Gbede da ke Karamar Hukumar Ijumu a jihar Kogi.

Bwala, a daya bangaren kuwa, kwararre ne a fannin shari’a, dan siyasa kuma manazarci kan harkokin jama’a.

Ya fito ne daga jihar Adamawa.

Bwala, a baya ya kasance jigo a jam’iyyar APC mai mulki, kafin ya sauya sheka zuwa jam’iyyar PDP saboda takarar Musulmi biyu da APC ta bai wa Bola Ahmed Tinubu da Kashim Shettima.