✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘Ba don karba-karba ba, da sai Arewa ta shekara 300 tana mulki’

Ya ce matukar PDP na son lashe zaben 2023, dole ta kai takara Arewa.

Wani jigo a jam’iyyar adawa ta PDP kuma tsohon Sanatan da ya wakilci mazabar Edo ta Kudu a Majalisar Dattijai, Roland Stephen Owie, ya ce in ba don tsarin karba-karba ba, yankin Arewacin Najeriya zai iya shekara 300 yana mulkin Najeriya.

Ya kuma gargadi jam’iyyarsu ta PDP da ta kai kujerar takarar Shugabancin Kasarta a 2023 zuwa Arewa, muddin tana son ta lashe zaben da ke tafe.

Sanata Roland, wanda ya taba zama Bulaliyar Majalisar Dattijai a 1999, ya bayyana hakan ne a cikin wata tattauanwarsa da jaridar Daily Trust, lokacin da yake tsokaci akan inda ya fi kamata a kai kujerar takarar a zabe mai zuwa.

A cewarsa, “Shi fa zabe magana ce ta yawan kuri’u, ka duba adadin mutanen da suka yi rijistar zabe a Najeriya, za ka ga yawan na kowacce yanki. Matukar ba ka da yawan kuri’u, to babu inda za ka je.

“Idan saboda son kai muka yi watsi da tsarin karba-karba, to ina mai tabbatar maka sai an shekara 300 Kudancin Najeriya bai shugabanci kasar nan ba.

“Za a sami zaman lafiya ne kawai in aka kwatanta adalci, a zahirin gaskiya ma babu tsarin karba-karba a Kundin Tsarin Mulkin PDP, amma an kawo shi ne don a sami maslaha, dalilin kenan ma da ya sa aka kawo Olusegun Obasanjo a 1999 don a danne kirjin Yarabawa saboda soke zaben Abiola da aka yi na 12 ga watan Yuni.

“Idan ka lissafa sosai, za ka ga cewa daga 1999 zuwa yau a karkashin mulkin PDP, yankin Kudu ya yi shekara 13 yana mulki, yayin da Arewa ya yi shekara uku kacal. Muddin PDP ta dauki takara a 2023 ta kai Kudu, to ta yi rashi adalci.

“PDP ce kadai jam’iyyar da ta yi amanna da hadin kan kasar nan, ya kamata kuwa ta kai takara Arewa a 2023.

“Amma a APC kuwa, tun da Arewa ta yi shekara takwas, babu laifi in sun kai takararsu Kudu,” inji Sanata Roland.