✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Babu Gwamnan da aka fi bincika a tarihin Najeriya sama da ni – Tinubu

Tinubu ya ce duk da binciken na kwa-kwaf da aka yi masa babu abin da aka samu

Tsohon Gwamnan Jihar Legas kuma dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Tinubu, ya ce babu wani Gwamna a tarihin Najeirya da ya fuskanci bincike kamar shi.

Ya ce duk da binciken na kwa-kwaf da aka yi masa babu abin da aka samu.

Tinubu ya bayyana hakan ne ranar Talata a tattaunawarsu da kafar BBC yayin ziyarar da ya kai London.

Dan takarar ya kuma bayyana ce-ce-ku-cen da ake yi game da dukiyarsa a matsayin hassada da kyashi.

Tinubu ya kuma ce a duk cikin ‘yan takarar Shugaban Kasa shi ne ya fi cancanta ya shugabanci Najeriya a zaben 2023 mai zuwa.

Ya kara da cewa, yana da yakinin muddin aka gudanar da sahihin zabe a 2023, shi ne zai lashe shi.

Tsohon Gwamnan ya ce, fannin tsaro da tattalin arziki su ne fannonin da zai bai wa muhimmanci muddin aka zabe shi Shugaban Kasa.