✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘Bai kamata Turanci da Lissafi su zama dole wajen samun gurbin karatu ba’

Ya ce kamata ya yi a rage yawan fifikon da ake ba takardu a Najeriya.

Shugaban Hukumar Shirya Jarabawa ta Kasa (NECO), Farfesa Ibrahim Dantani Wushishi ya yi kira da a daina amfani da tsarin tilasta samun sakamako a darussan Turanci da Lissafi kafin samun gurbin karatu a manyan makarantun Najeriya.

Ya bayyana haka ne yayin da yake jawabi a taron Kungiyar Makarantun Islamiyyah a Minna, babban birnin Jihar Neja ranar Asabar.

Ya kuma yi kira da a kafa kotu ta musamman don hukunta masu magudin jarrabawa domin a cire tarnakin da ake fuskanta wajen gurfanarwa da kuma hukunta masu aikata laifin satar jarabawar.

Farfesa Wushishi, a cikin makalar da ya gabatar mai taken: “Yadda za a magance magudin jarrabawa domin ci gaban kasa”, ya ce, “Ya kamata Gwamnatin Tarayya ta rage yawan tasirin da take ba takardu a kan komai a kasar nan, wajen tantancewa da kuma ba da sakamako ga dalibai da ma’aikata.”

Shugaban na NECO ya lura cewa tsare-tsare da manufofin gwamnati a kan harkar ilimi na bukatar garanbawul, inda ya ce akwai bukatar samar da isassun kayan aiki a makarantun gwamnati don inganta harkar koyo da koyarwa.

A cewarsa, Jihohin da aka fi samun matsalar magudin jarrabawa sun hada da Bauchi da Borno da Kano da Kebbi, musamman a cikin shekaru biyar da suka gabata.

Sai dai ya zargi iyaye da malamai da ma tsarin gudanar da makamantun a matsayin ummul’aba’isun tabarbarewar al’amura.

Ya ce ya zama wajibi a hada karfi da karfe wajen magance matsalar ilimi a Najeriya.