✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Bam ya hallaka mutum 4, ya jikkata wasu 38 a Turkiyya

Fashewar ta auku ne a wani waje mai matukar cunkoson jama'a

Wani abin fashewa da ake kyautata zaton bam ne ya tarwatse a wata gadar da mutane ke bi a birnin Istanbul na kasar Turkiyya, inda ya hallaka mutum hudu, wasu 38 kuma suka jikkata.

Bam din ya tashi ne a kan gadar da ke kan titin Istiklal a unguwar Taksim, da misalin karfe 4:20 na yammacin Lahadi, wato misalin karfe 2:20 a agogon Najeriya.

Wasu hotunan inda lamarin ya faru sun nuna yadda motocin daukar marasa lafiya da na kashe gobara da kuma na ’yan sanda ke ta kokarin aikin ceto a wajen.

Har zuwa yanzu dai ba a kai ga gano musabbabin fashewar ba.

Wakiliyar gidan talabijin na Aljazeera a Istanbul, Sinem Koseoglu, ta ce ana zargin fashewar ba za ta rasa nasaba da kunar bakin wake ba, kodayake har yanzu babu wata sanarwa a hukumance a ka hakan.

Sinem ta kuma ce harin ya zo wa mutane da dama da ba-zata, sakamakon babu wani gargadi gabanin hakan kan barazanar kai hari.

Sai dai ta ce an tsaurara matakan tsaro matuka a yankin. (Aljazeera)