✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Basarake ya rantse da Alkur’ani a masallaci cewa ba ya taimaka wa ’yan bindiga

“Matukar ina taimaka musu, kada Allah ya sa na kai wani satin,” inji shi.

A Jihar Sakkwato, wani basarake ya mike a masallacin Juma’a sannan ya rantse da Alkur’ani mai girma kan cewa ba ya taimaka wa ayyukan ’yan bindiga ta kowacce fuska a masarautarsa.

Basaraken, wanda shi ne Hakimin Isa, kuma Sarkin Gobir din Isa, Alhaji Nasir Ahmad ya rantse da Alkur’anin ne a masallaci biyo bayan zargin da wasu mazauna yankin ke yi masa na alaka da ’yan ta’adda.

Ko a ranar Litinin din da ta gabata sai dai wasu fusatattun mazauna yankin suka kai hari kan fadar Hakimin bayan sun zarge shi da ba bata-gari mafaka.

Rahotnanni sun ce Hakimin ya mike a Masallacin Juma’ar garin jim kadan kafin fara Salla sannan ya rantse cewa ba ya taimaka wa ayyukan ta’addanci.

“Idan na taba taimaka wa kowanne irin hari a yankina, ko na taba ba ’yan bindiga bayanai a kan ayyukan sojoji a masarautata, kada Allah ya sa na kai wani makon,” inji shi.

A wani faifan bidiyon Hakimin dai wanda ya karade gari musamman a kafafen sada zumunta na zamani, an jiyo Hakimin na cewa ya fi kowa a yankin jin takaicin hare-haren da ake kai wa jama’arsa.