✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Batanci: Tambuwal ya cire dokar hana fita a Sakkwato

Tambuwal ya mika godiyarsa ga al'ummar jihar dangane da hadin kan da suka bai wa dokar.

Gwamna Aminu Waziri Tambuwal ya janye dokar hana fita da ya sanya a birni da kewayen Jihar Sakkwato.

Janyewar wadda ta fara aiki nan take na zuwa ne a matsayin matakin da gwamnatin jihar ta dauka bayan tattaunawa da neman shawarwarin hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki.

Gwamna Tambuwal ya gargadi mazauna jihar da suka kasance masu yi wa doka da’a sannan su zama jakadu na zaman lafiya a kowane lokaci.

Tsohon Kakakin Majalisar Wakilan Najeriyar ya jaddada muhimmancin hadin kai da zama cikin aminci a tsakanin al’ummar jihar.

Kazalika, ya haramta duk wata zanga-zanga a jihar har sai abin da hali yayi.

Gwamnan ya kuma mika godiyarsa ga al’ummar jihar dangane da hadin kan da suka bai wa dokar hana fita da aka sanya kwanaki kadan da suka gabata.

A safiyar Asabar ce wasu matasa suka soma wata zanga zanga wadda daga baya ta soma rikidewa zuwa tarzoma, abinda ya sa gwamnatin Jihar Sakkwato ta saka dokar hana fita ta tsawon sa’a 24.

Gwamnan ya sanya dokar ta-bacin ne domin shawo kan tashe-tashen hankula da suka biyo bayan kisan da aka yi wa wata dalibar Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari da aka zarga da yin batanci ga Fiyayyen Halitta, Annabi Muhammad (SAW).