✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Belin Abduljabbar: Kotu za ta yanke hukunci ranar 31 ga Maris

Kotu ta dage sauraron bukatar belin malamin da mako biyu.

Babbar Kotun Musulunci da ke zamanta a Kofar Kudu a Jihar Kano ta sanya 31 ga watan Maris, 2022 a matsayin ranar yanke hukunci a kan bukatar ba da belin Sheikh Abduljabbar Kabara da lauyansa ya gabatar mata.

Ana zargin Abduljabbar Kabara ne dai da laifin yin batanci ga Annabi Muhammad (SAW) da kuma tayar da hankalin jama’a.

Da yake gabatar da bukatar belin, lauyan malamin ya yi wa kotu alkawarin cewa za su bi dukkanin sharuddan da za a gindaya musu.

Sai dai lauyoyin masu shigar da kara karkashin jagorancin Barista Saida Suraj sun nemi kotu ta yi watsi da bukatar bisa la’akari da girman laifin da ake tuhumar wanda ake zargi, wanda a cewarsu zai iya kai ga yanke mishi hukuncin kisa, karkashin dokar Kundin laifufuka ta Jihar Kano  ACJL 171 (1).

“Baya ga haka kuma, a yanzu da ake gabar kariya babu wani dalili da zai sa a nemi belin wanda ake kara; Haka kuma ba mu ji an ambaci wani dalili mai karfi da zai sa a bayar da  belin ba.” inji shi.
Shi kuwa lauyan wanda ake kara, cewa ya yi kotu tana da hurumin bayar da belin wanda ake zargi kasancewar har yanzu ba ta kama wanda ake zargi da laifin ba, dogaro da sashe na 36 (6) na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya.

Hakan ya sa alkalin kotun, Mai Shari’a Sani Sarki Yola ya dage zaman da mako biyu, zuwa ranar 31 ga watan Maris don jin ra’ayin kotun game da batun bayar da belin.